IQNA

Wabiyawa Na Da Hannu Wajen Samar Da Kungiyar Ta’addanci Ta Daesh

20:31 - August 07, 2015
Lambar Labari: 3339770
Bangaren kasa da kasa, limamin masallacin Sheikh Zayid a birnin Abu Dhabi ya bayyana cewa wasu daga masu isar da sakon wahabiyanci suna da hannu wajen samar da kungiyar ta’addanci ta Daesh.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Arabi 21 cewa, Wasim Yusuf shi ne limamin masallacin Sheikh Zayid a birnin Abu Dhabi ya fadi cewa wasu daga wahabiyawa musamman Uraifi da Salman Audah suna da hannu wajen yada tunanin  kungiyar ta’addanci a tsakanin larabawa.

Ya ce wani daga cikin masu tabligin wahabiyanci mai suna Hammud Al-umari ya kasance daya daga cikin masu wannan tunani tare da yada shi, kma an tsare shi a gidan Kason Abu Ghoraib da Al-taji a kasar Irakia  shekara ta 2013, bayan ya fito kuma ya ci gaba da goyon bayan Abubakar Albaghdadi.

Wasim Yusuf ya kara da cewa, Al-uraifi yana goyon bayan akidar Daesh ta ta’addanci, haka nan kuma Salman Audah shi ma yana nuna goyon bayansa da hakan a fili.

3339662

Abubuwan Da Ya Shafa: Wabiyyah
captcha