IQNA

Borkina Faso Ta Sanar Da Zaman Makoki Na Kwanaki Ukku Kan Mutuwar Mahajjatanta A Mina

21:30 - October 15, 2015
Lambar Labari: 3385862
Bangaren kasa da kasa, Gwamnatin kasar Borkina Faso ta bada sanarwan makoki na kwanaki uku farawa daga ranar gobe idan Allah ya kai mu.


Kamfanin dilalncin labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Shafaqna cewa, a yau ne gwamnatin kasar Borkina Faso ta bada sanarwan makoki na kwanaki uku a fadin kasar wanda zai fara daga ranar gobe Juma’a.

Bayanin ya ci gaba da cewa sanadiyyar rasuwar mahajjatan kasar 22 da aka tabbatar da mutuwarsu a turmutsutsin ranar sallar layyar da ta gabata.



Kamfanin dillancin labaran faransa  ya ce gwamnatin kasar ta bada wannan sanarwar ce bayan taron majalisar ministocin kasar a jiya laraba. Ta kuma kara da cewa ya zuwa ranar sha uku ga oktoba da muke ciki, mahajjatan kasar 22 aka tabbatar da mutuwarsu.



Sannan har yanzun akwai wasu guda 9 da suka bace banda haka sanarwar ta kara da cewa akwai wasu mahajjan 15 da suka rasu don rashin lafiya a lokacin aikin hajji na shekara da muke ciki.



3385777

Abubuwan Da Ya Shafa: Burkina Faso
captcha