IQNA

Karfafa Koyarwar Musulunci Ita Ce Babbar manufar Radio Kur’an

23:40 - October 04, 2016
Lambar Labari: 3480823
Bangren kasa da kasa, daraktan radiyo kur’an a kasar Algeria ya bayyana manufar shirin gidan radiyon da cewa ita ce yada koyarwar kur’ani.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalt daga shafin sadarwa na yanar gizo na radioalgerie.dz cewa, Hamadi Isa babban daraktan radiyo kur’an a kasar Algeria ya bayyana manufar shirye-shiryensu a gidan radiyon da cewa yana da alaka ne da isar da sakon zaman lafiya na addinin muslunci ga al’ummar duniya.

Ya ce tun kimanin shekaru 25 da suka gabata ne aka bude wannan gidan radiyo, wanda yake gabatar da shirinsa kan lamurra da suka shafi kur’ani da kuma koyarwarsa, kafin daga bisani a bude bangaren talabijin wanda shi ma yake gabatar da irin wadannan shirye-shirye.

Daga cikin muhimman abubuwan da ake mayar da hankalia kansu shi ne yadda ya kamata musulmi su zauna da juna tare dasamun fahimta, da kuma zama lafiya da sauran mabiya addinai, kamar yadda musuunci ya koyar, haka nan kuma ana taba batutuwa da suka shafi tattalin arziki, zamantakewa, al’adu da sauransu, duk a mahanga ta addinin muslunci.

3535360


captcha