Kamfanin dillancin labaran IQNA, Sheikh Isma’il Du’a, shugaban majalisar musulmin kasar Uganda ya aike da wata wasika zuwa ga jakadan kasar Iran a Uganda da ke birnin kampala, inda a cikin wasikar ya isar da sakon ta’aziyyar shahadar janar Kasim Sulaimani.
A cikin matanin wasikar malamin ya ci gaba da cewa; kisan gillar da aka yi Kasim Sulaimani lamari ne da ya shafi dukkanin musulmi baki daya, domin kuwa shi mutum ne da ya kasance a sahun gaba wajen kare martabar addinin muslunci.
Haka nan kuma malamin ya ce a madadin dukaknin musulmin kasar Uganda, suna kara jaddada kira kan wajabcin hadin kan al’ummar msuulmi, domin hakan shi ne a cewarsa shi ne kadai mafita guda da ta rage ga msuulmi a halin yanzu.
A cikin wanann mako majalisar musulmin kasar ta Uganda ta aike da sako ga dukkanin liammai na jihohi 8 a kasar, kan su yi Allawadai da kisan Kasim Sulaimania cikin hudubobin Juma’a.