IQNA

23:01 - November 18, 2020
Lambar Labari: 3485379

Tawagar Bahrain Ta Isa Isra'ila Domin Ganawa Da Jami'an Gwamnatin Yahudawa

Tehran (IQNA) tawagar gwamnatin kasar Bahrain ta fara gudanar da wata ziyara a hukumance a  Isra’ila.

Tawagar Bahrain Ta Isa Isra'ila Domin Ganawa Da Jami'an Gwamnatin Yahudawa

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Bahrain ta bayar da bayanin cewa, wata tawagar gwamnatin kasar karkashin jagorancin ministan harkokin wajen Abdullatif Bin Rashid Azayani ta isa birnin Tel Aviv na Isra’ila a yau Laraba.

Bayanin ya ce waannan ita ce ziyara ta farkoa  hukumance da tawagar gwamnatin Bahrain ta fara kaiwa a Isra’ila, kuma nan gaba za a ci  gabada ganin irin wannan ziyara tsakanin jami’an gwamnatocin Isra’ila da na Bahrain.

Ministan harkokin wajen gwamnatin yahudawan Isra’ila Gabi Ishkinazi ne dai da kansa ya rabi tawagar ta gwamnatin Bahrain a Telaviv, inda ya bayyana ziyarar tasu da cewa ta tarihi ce a  tsakainsu.

To sai dai a daya bangaren al’ummomin kasar Bahrain suna ta yin tofin Allah tsine dangane da wannan ziyara, inda suke ta yin bayanai a shafukan sadarwa na zumunta, kan cewa wannan ziyara ba da sunansu ake gudanar da ita ba.

Gwamnatin Bahrain ta sanar da kulla alaka tsakaninta da Isra’ila ne tun a cikin watan da ya gabata, amma majiyoyin kafofin yada labaran gwamnatin Isra’ila sun bayyana cewa akwai alaka ta boye tsakanin Israila da Bahrain tun kusan shekaru talatin da suka gabata, a yanzu dai alakar ta fito fili ne a hukumance.

3936057

 

captcha