IQNA

An bayyana sunayen wadanda suka lashe gasar kur'ani ta kasa da kasa ta Masar

14:09 - December 11, 2024
Lambar Labari: 3492368
IQNA - A yayin wani biki, an bayyana sunayen wadanda suka lashe gasar kur’ani ta kasa da kasa ta Masar karo na 31 tare da karrama wadanda suka yi nasara.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, shafin yada labarai na Al-Masri Al-Youm ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Masri Al-Youm cewa, a daren jiya da dare ne Osama Al-Azhari, ministan kula da harkokin addini na kasar Masar ya bayyana sunayen wadanda suka lashe gasar kur'ani ta kasa da kasa karo na 31 a kasar Masar.

Wannan gasa wadda aka fara a ranar Asabar 7 ga watan Disamba a karkashin kulawar ma'aikatar kula da harkokin addini ta kasar Masar, ta kare ne a ranar 20 ga watan Disamba tare da rufe gasar da kuma bayyana sakamakon bayan sallar magriba a masallacin da cibiyar al'adu ta Masar a sabon tsarin gudanarwa babban birnin kasar.

 

 

4253566

 

captcha