Taron zai samu halartar tsohon shugaban jami’ar Azhar Ibrahim Al-Hodhud da tsohon shugaban tsangayar koyar da harshen larabci na birnin Alkahira Salah Ashour da kuma Reza Abdel Salam tsohon shugabar gidan rediyon kur’ani na kasar Masar ne za su jagoranci taron.
A dangane da haka Abdul Moneim Fouad babban mai kula da ayyukan kimiyya na farfajiyar Azhar na masallacin Al-Azhar ya bayyana cewa: Wannan taro wata muhimmiyar dama ce ta yin tunani a kan ayoyin kur'ani da yin la'akari da ma'anonin su, kuma hakan yana bude sabbin kofofin bincike kan mu'ujizar kur'ani.
Ya kara da cewa: Wannan taron karawa juna sani zai yi tasiri wajen karfafa fahimtar addini da al'adu na mahalarta taron, tare da mai da hankali kan masallacin Al-Aqsa, da kuma yin tunani mai zurfi kan nassosin addini.
Dangane da haka, Hani Odeh mai kula da babban masallacin Azhar ya bayyana jin dadinsa da gudanar da taron tare da jaddada muhimmancin mu'ujizar kur'ani wajen siffanta al'ummar musulmi.
Hani Odeh ya kara da cewa: "Ana gudanar da wadannan tarurrukan lokaci-lokaci a ranakun Lahadi a kowane mako, kuma kungiyar kwararrun masana da malamai suna gabatar da jawabai."